Table Of Content1436
KITABUT TAUHID
>اسولها<
Wallafar:
Sheikh: Salihu bn Fauzan bin Abdallahil Fauzan.
Fassarar
Aliyu Muhammad Sadisu
Wanda ya duba:
Attahiru Bala Dukku
1436
ديحولتا باتك
نازوفلا الله دبع نب نازوف نب حلاص .د
:ةجمرت
سداس دممح علي
:ةعجارم
وكد لاب رهاطلا
Kitabut Tauhid
1
Gabatarwa Mai Fassara
Da sunan Allah mai yawan rahama mai yawan jinkai.
Dukkan godiya ta tabbata a gareshi, kuma tsira da
amincin Allah su tabbata ga Annabi Muhammad da
iyalanshi da kuma sahabbanshi baki-daya.
Bayan haka, wannan fassarar littafin “Kitabut Tauhid”
ne, wanda Shehun malami Dr. Saleh bin Fauzan bin
Abdallah Alfauzan ya wallafa, wannan malami fitaccan
malami ne mamba ne a majalisar manyan malamai ta
kasar Saudi Arebiya, kuma mamba a kwamitin dindindin
na fatawa da kuma bincike akan ilimi.
Wannan littafi na Tauhidi da wannan malami ya wallafa
ya taba bangarori da dama wadanda ake matukar neman
bayanan su a daidai wannan lokaci, zaka iya cewa littafin
ya zo ne a daidai lokacin da ake matukar bukatarsa.
Mawallafin littafin ya fara kawo mukiddima ne sannan
ya biyo shi da babi-babi har guda hudu, sannan akar
kashin kowanne babi akwai fasali-fasali da malam ya
kawo. Babi na farko yana kunshe ne da fasali biyar, a
yayinda babi na biyu kuma yake kunshe da fasali-fasali
Kitabut Tauhid
2
har goma sha-daya, shi kuwa babi na uku yana dauke ne
da fasali-fasali har guda shida, ayayin da babi na karshe
wato babi na hudu yake dauke da fasalai har guda hudu.
Wannan littafi kamar yadda sunansa yake ‘Kitabut
Tauhid’, kuma haka na Shehun malamin nan wato
Sheikh Muhammad dan Abdulwahhab yake da ‘Kitabut
Tauhid’ to amma sun yi tarayyane a suna amma sun sha
banban a irin bayanan da suke dauke da shi, duk da
bayanaine na tauhidi da kowanne yake da shi, saidai
bangarorin da kowa ya dauka ya yi bayani daban-daban
ne, saboda haka ana bukatar ka hada su duka ka mallake
su, Allah ya anfanar da mu da su baki-daya.
Lalle akwaimatukar bukatar a karantar da wannan littafi
a makarantu da masallatai da kuma wuraran fadakarwa a
kuma yada shi, saboda matukar muhimmancin da yake da
shi da kuma yadda ya tabo wadansu bayanai da ake
aikatawa a wannan lokacin da suke bukatar irin
wadannan malamai su yi bayaninsu.
Allah ya sakawa wannan malami da kuma wadanda suka
yada wannan littafi Allah ya saka musu da alheri.
Kitabut Tauhid
3
Dukkan godiya ta tabbata ga Allah, tsira da amincin
Allah su tabbata ga Annabi Muhammad da iyalanshi
da kuma sahabbanshi baki daya.
Mai fassara;
Aliyu Muhammad Sadisu,
Minna,
Nigeria.
Email. [email protected]
***** ****** ******
ميحرلا نمحرلا الله مسب
Gabatarwar Mawallafi:
Da sunan Allah mai yawan rahama mai yawan jinkai,
dukkan godiya ta tabbata ga Allah Ubangijin halittu, tsira
Kitabut Tauhid
4
da amincin Allah su tabbata ga Annabinsa mai gaskiya
kuma amintacce Annabimmu Muhammad da kuma
iyalanshi da sahabbanshi baki daya, bayan haka:
To wannan littafi an wallafa shi ne akan ilimin tauhidi,
kuma hakika na yi la’akarin takaita shi ta yadda lafuzan
za su yi sauki, kuma na ciro bayananne daga
manyamanyan littattafai masu yawa daga cikin littattafan
manyan malamammu musammamma littattafai Shekhul
Islam Ibnu Taimiya, da littafan Shehun malami Ibnu
Kayyim da kuma littattafan Shekhul Islama Muhammad
dan Abdulwahhab da na almajiransa jagororin wannan
Da’awah mai tarin albarka.
Kuma yana daga cikin abinda kwatakwata babu wani
kokwanto akai shi ne: Lalle ilimin sanin ‘Akidar
Musulunci’ shi ne babban tushen da ya fi cancantar a
kula da shi da wajan koyo da kuma koyarwa da kuma
aiki da shi, domin da shi ne ayyuka za su zama karbabbu
a wurin Allah, ta zama mai amfani ga wadanda su ka yi
su, musamman a wannan zamani da ake fama da akidu iri
daban-daban; Akidun masu ilhadi, ga akidun sufaye ga
Kitabut Tauhid
5
maguzawa masu bautar kabari, ga kuma akidu na bidi’o’I
da suka sabawa karantarwar Annabi . Dukkanin
wadannan akidune masu matukar hadari muddin mutum
musulmi bai kasanke yana da shiri na kyakkyawar akidah
ba wacce ta ginu akan littafin Allah da Sunnar Annabinsa
da kuma abinda magabatan wannan al’umma na
kwarai suka kasance kai ba to kan in ya yi wasa tuni
wadancan akidu za su masu batarwa za su debe shi.
Wannan ko yana cikin abinda zai sa a bada cikakkiyar
kulawa akan karantar da ingantacciyar akida ga ‘ya’yan
musulmi daga tushenta na asali.
Allah ya yi dadin tsira ga Annabimmu Muhammad da
iyalanshi da kuma sahabbanshi.
Mawallafi.
BABI NA FARKO:
Karkatar da aka samu a rayuwar Dan’adam,
da kuma takaitaccan bayani akan kafirci da
kuma ilhadi da shirka da munafunci.
Wannan ko ya kunshi wadannan fasalin ne:
Kitabut Tauhid
6
Fasali Na Farko: Karkata a rayuwar dan’adam.
Fasali Na Biyau: Shirka, bayaninta da nau’ukanta.
Fasali Na Uku: kafirci, bayaninsa da nau’ukansa.
Fasali Na Hudu: Munafunci, bayaninsa da kuma
nau’ukansa.
Fasali Na Biyar: Hakikanin abinda ake nufi da
wadannan abubuwan:
(1) Jahiliyyah.
(2) Fasikanci.
(3) Bata.
(4) Riddah, karkasuwarta da hukunce hukuncenta.
**** ***** *****
Kitabut Tauhid
7
Fasali Na Farko:
Karkata a rayuwar dan’adam.
Allah madaukakin sarki ya halicci halitta ne domin su
bauta masa, kuma ya sawwake musu abinda zai taimaka
musu na arzikinsa, Allah madaukakin sarki yana cewa:
ﭿ ﭾ ﭽ ﭼ ﭻ ﭺ ﭹ ﭸ ﭷ ﭶ ﭵ ﭴ ﭳ ﭽ
:تايراذلاﭼ ﮋ ﮊ ﮉ ﮈ ﮇ ﮆ ﮅ ﮄ ﮃ ﮂ ﮁ ﮀ
٦٥ – ٦٥
Ma’ana:“Kuma ban halicci aljan da mutum ba sai domin
kawai su bauta mini. Bana neman wani arziki daga gare
su kuma bana bukatar da su ciyar da ni. Lalle Allah shi ne
kadai mai azurtawa kuma maba’abocin karfi sosai”.
Suratuz Zariyat, aya ta:56-58.
Mutum a halittar da Allah ya yi masa zai bautawa Allah
ne shi dakai inda za’a bar shi, ya zama mai son Allah ya
na bauta masa ba ya yi ma sa shirka, sadai abinda ya
bata wannan (dabi’ar) kuma yake karkatar da ita shi ne
Kitabut Tauhid
8
abin shedanun aljanu da na mutane su ke kawata mata
na abinda sashin su yake yi wa sashi wahayi na
kawatacciyar Magana kawai don rudi, shirka wata aba ce
da ta zo daga baya kuma ta kutsa kai ga halittar da Allah
ya yi wa mutum, Allah madaukakin sarki yana cewa:
ﯠ ﯟﯞ ﯝ ﯜ ﯛ ﯚ ﯙ ﯘﯗ ﯖ ﯕ ﯔ ﭽ
٠٣ :مورلا ﭼﯣ ﯢ ﯡ
Ma’ana:“To, ka tsayar da fuskarka ga wannan addini
kana mai kaucewa shirka, halittar Allah wacce ya halicci
mutane a kan ta, babu mai canza halittar Allah”. Suratur
Rum, aya ta: 30.
Kuma Ma’aikin Allah ya ce:
ُُو ُأُ ُه ُنار ُُص ُن ُ يُ ُو ُأُ ،ُه ُناُد وُ ُه ُ يُ ُهاو ُُ ب ُأ ُفُ ،ُ ةر ُ ُطُف ُل ُاُ ى ُلُع ُ ُد ُلو ُيُ ُد و ُلوُ ُم ُ ُل ُك ((
ُ .ملسموُيراخبلاُهاورُ.))ُهُناُسُج ُي
Ma’ana:“Dukkan abin haihuwa ana haihuwarsa ne akan
musulunci, to iyayan shi ne su ke yahudantar da shi, ko
su Nasarantar da shi (kiristan da shi) ko su majusantar
Description:kana mai kaucewa shirka, halittar Allah wacce ya halicci mutane a kan ta, babu mai canza halittar Allah”. Suratur. Rum, aya ta: 30. Kuma Ma'aikin